Acts 5

Ananiyas da Saffiratu

1To wani mutum mai suna Ananiyas tare da matarsa Saffiratu, shi ma ya sayar da wata mallakarsa. 2Da cikakken sanin matarsa ya ajiye sashi daga cikin kuɗin don kansa, ya kuma kawo sauran ya ajiye a sawun manzanni.

3Sai Bitrus ya ce, “Ananiyas, ta yaya Shaiɗan ya cika zuciyarka haka da ka yi wa Ruhu Mai Tsarki ƙarya ka kuma ajiye wa kanka sauran kuɗin da ka karɓa na filin? 4Ba naka ba ne kafin ka sayar da shi? Bayan da ka sayar da shi kuma, kuɗin ba naka ba ne? Me ya sa ka yi tunanin yin irin wannan abu? Ba mutum ne ka yi wa ƙarya ba, Allah ne ka yi masa.”

5Da Ananiyas ya ji wannan, sai ya fāɗi ya mutu. Sai babbantsoro kuwa ya kama duk waɗanda suka ji abin da ya faru. 6Sai samari suka zo gaba, suka naɗe gawarsa, suka fitar da shi suka je suka binne.

7Bayan kusan awa uku, sai matarsa ta shigo, ba da sanin abin da ya faru ba. 8Bitrus ya tambaye ta, ya ce, “Gaya mini, kuɗin da yake da Ananiyas kuka sayar da filin ke nan?”

Ta ce, “I, haka ne muka sayar.”

9Bitrus ya ce mata, “Ta yaya kuka yarda ku gwada Ruhun Ubangiji? Duba! Sawun mutanen da suka binne mijinki suna bakin ƙofa, za su kuwa ɗauke ki zuwa waje ke ma.”

10Nan take ta fāɗi a ƙafafunsa ta mutu. Sai samarin suka shigo ciki, suka kuwa same ta matacciya, suka ɗauke ta suka kai ta waje suka binne ta kusa da mijinta. 11Babbantsoro ya kama dukan ikkilisiya da kuma duk wanda ya ji game da abubuwan nan.

Manzanni Sun Warkar da Mutane da Yawa

12Manzannin suka yi ayyukan da alamu masu banmamaki masu yawa a cikin mutanen. Dukan masu bi kuwa sukan taru a Shirayin Solomon. 13Ba wanda ya yi karambanin shiga cikinsu, duk da haka mutane suna girmama su ƙwarai. 14Duk da haka, maza da matan da suke gaskata ga Ubangiji sai ƙaruwa suke, suka kuma ƙaru a yawa. 15A sakamakon haka, mutane suka kawo marasa lafiya a tituna suka kwantar da su a kan gadaje da tabarmai domin aƙalla inuwar Bitrus za ta bi kan waɗansunsu yayinda yake wucewa. 16Jamaʼa ma suka tattaru daga garuruwa kewaye da Urushalima suna kawo marasa lafiyarsu da kuma waɗanda mugayen ruhohi suke damun su, dukansu kuwa suka warke.

An Tsananta wa Manzanni

17Sai babban firist da dukan abokan aikinsa, waɗanda suke na ƙungiyar Sadukiyawa suka cika da kishi. 18Suka kama manzannin suka sa su a kurkukun da ake sa kowa da kowa. 19Amma da dare wani malaʼikan Ubangiji ya buɗe ƙofofin kurkukun ya fitar da su. 20Ya ce, “Ku je ku tsaya a filayen haikali ku sanar wa mutane cikakken saƙon wannan sabon rai.”

21Da gari ya waye, sai suka shiga filayen haikali, yadda aka faɗa musu, suka kuwa fara koyar da mutane.

Saʼad da babban firist da abokan aikinsa suka iso, sai suka kira Majalisa gaba ɗaya-dukan dattawan Israʼila-suka kuma aika kurkuku a zo da manzannin.
22Amma da dogarawan suka iso kurkukun, ba su same su a can ba. Saboda haka suka dawo suka ba da labari, suka ce, 23“Mun iske kurkukun a kulle sosai, da masu gadi suna tsaye a bakin ƙofofin; amma da muka buɗe su, sai muka tarar ba kowa a ciki.” 24Da jin wannan labari, sai shugaban masu gadin haikali da manyan firistocin suka ruɗe, suna tunanin abin da wannan alʼamari zai zama.

25Sai wani ya zo ya ce, “Ga shi! Mutanen da kuka sa a kurkuku suna tsaye a filayen haikali suna koya wa mutane.” 26Da wannan, shugaban ya tafi tare da dogarawansa suka kawo manzannin. Sun kawo su amma fa ba ƙarfi da yaji ba, don suna tsoro kada mutane su jajjefe su da duwatsu.

27Da suka kawo manzannin, sai suka sa su suka bayyana a gaban Majalisar don babban firist ya tuhume su. 28Ya ce, “Mun kwaɓe ku da gaske kada ku ƙara koyarwa cikin wannan suna, duk da haka kun cika Urushalima da koyarwarku, har ma kuna so ku ɗora mana laifin jinin mutumin nan.”

29Bitrus da sauran manzannin suka amsa suka ce: “Dole ne mu yi wa Allah biyayya a maimakon mutane! 30Allahn kakanninmu ya ta da Yesu daga matattu-wanda kuka kashe ta wurin ratayewa a bisan itace. 31Allah ya ɗaukaka shi zuwa hannun damansa a matsayin Yerima da Mai Ceto don ya kawo tuba da gafarar zunubai ga Israʼila. 32Mu shaidu ne ga waɗannan abubuwa, haka kuma Ruhu Mai Tsarki, wanda Allah ya ba wa waɗanda suke yin masa biyayya.”

33Da suka ji haka, sai suka yi fushi suka so su kashe su. 34Amma wani Bafarisiyen da ake kira Gamaliyel, wani malamin doka, wanda dukan mutane ke girmamawa, ya miƙe tsaye a Majalisar ya umarta a fitar da mutanen waje na ɗan lokaci. 35Saʼan nan ya yi musu jawabi ya ce: “Mutanen Israʼila, ku yi kula da kyau da abin da kuke niyyar yi wa mutanen nan. 36Kwanan baya, Teyudas ya ɓullo, yana cewa wai shi wani mutum ne, kuma wajen mutane ɗari huɗu suka bi shi. Aka kuwa kashe shi, dukan masu binsa kuwa suka watse, kome ya wargaje. 37Bayansa, Yahuda mutumin Galili ya ɓullo a kwanakin ƙidaya, ya jagoranci mutane cikin tawaye. Shi ma aka kashe shi, dukan mabiyansa kuma aka watsar da su. 38Saboda haka, a wannan batu na yanzu, ina ba ku shawara: Ku ƙyale mutanen nan! Ku bar su su tafi! Gama in manufarsu ko ayyukansu na mutum ne, ai, zai rushe. 39Amma in daga Allah ne, ba za ku iya hana waɗannan mutane ba, za ku dai sami kanku kuna gāba da Allah ne.”

40Jawabinsa ya rinjaye su. Suka kirawo manzannin suka sa aka yi musu bulala. Saʼan nan suka kwaɓe su kada su ƙara magana a cikin sunan Yesu, suka kuma bar su suka tafi.

41Manzannin suka bar Majalisar, suna farin ciki domin an ga sun cancanta a kunyata su saboda Sunan nan. 42Kowace rana, a filayen haikali da kuma gida gida, ba su fasa koyarwa da kuma shelar labari mai daɗi cewa Yesu shi ne Kiristi ba.

Copyright information for HauSRK